
Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta sanya dokar hana zirga-zirgar mutane da ababen hawa a jihar yayin zaben kansiloli da aka shirya gudanarwa a ranar Asabar 15 ga Fabrairu, 2025.
A wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Aliyu Abubakar ya fitar a Katsina ya tabbatar da faruwar lamarin.
Sanarwar ta kara da cewa, “Saboda zaben kananan hukumomin da aka shirya gudanarwa a ranar Asabar 15 ga watan Fabrairu, 2025, za a takaita zirga-zirgar mutane da ababen hawa daga karfe 0600 – 1600 a cikin jihar.
“An samar da wannan matakin ne domin tabbatar da doka da oda, da kuma tabbatar da tsaron al’ummar da za su kada kuri’a ba tare da tsangwama ba.
“Kwamishanan ‘yan sandan jihar Katsina, CP Allyu Abubakar Musa, ya bukaci mazauna jihar da masu ruwa da tsaki a jihar da su bi wannan dokar ta hana zirga-zirga domin inganta gudanar da zabe cikin kwanciyar hankali da lumana, an kuma yi isassun tsare-tsare na tsaro domin tabbatar da dokar hana zabe da kuma tabbatar da tsaron duk masu zabe da jami’an zabe.
“Ya kuma yi kira ga wadanda suka cancanci kada kuri’a da su fito su shiga a dama da su a gudanar da zaben tare da gudanar da ayyukansu na al’umma cikin lumana da kwanciyar hankali.
“Ga duk wani gaggawa, ana ƙarfafa jama’a da su yi amfani da layukan gaggawa na umarni;
08156977777;
09022209690;
07072722539.”