
Sabon shugaban ma’aikata na gwamnan jihar Katsina Dr Dikko Umar Radda, Alh Abdulqadir Mamman Nasir ya yi kira ga ‘yan jarida masu aiki a jihar da su tabbatar da Balance rahoton ayyukan gwamnati.
Alh Abdulqadir Nasir ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan rantsar da shi da gwamnan jihar ya yi.
Shugaban ma’aikatan wanda ya yi alkawarin aiwatar da manufar bude kofa, ya yi kira ga ‘yan jarida da su rika neman karin haske kan ayyukan gwamnati kai tsaye daga ofishinsa.
Alh Abdulqadir Nasir ya jaddada cewa masu aikin yada labarai suna taka rawar gani wajen tsara manufofi da shirye-shiryen gwamnati, don haka akwai bukatar a kula da su da kyau.
Shugaban ma’aikatan ya bayyana godiya ga Gwamna Dr Dikko Radda bisa wannan nadin, ya kuma yi alkawarin yin iya bakin kokarin sa don ci gaban jihar.
Ya kuma yi kira ga jama’a da su ci gaba da yi wa gwamnati addu’ar samun nasara a wannan gwamnati da kuma zaman lafiya a jihar.