Sanata ‘Yar’Adua Ya Tallafawa Manoman Rani a Dutsin-Ma

Da fatan za a raba

A karo na biyu cikin kasa da mako biyu Sanata Abdulaziz Musa ‘Yar’adua ya tallafawa manoman ban ruwa a karamar hukumar Dutsin-ma ta jihar Katsina.

Ya tallafa musu da takin zamani da injinan fanfo da feshi.

Sanata ‘Yar’aduwa wanda ke rike da sarautar gargajiya ta Mutawallen Katsina shi ne Sanata mai wakiltar Katsina ta tsakiya a majalisar dattawan tarayyar Najeriya.

Shi ne kuma shugaban kwamitin majalisar dattawa kan sojoji sannan kuma shugaban kungiyar Sanatocin Arewa.

Idan dai za a iya tunawa, kasa da mako biyu Sanata ‘Yar’adua ya raba wa manoman noman rani na Dutsin-Ma buhunan taki.

Malam Zailani Muhammad Jikan Maigari ko’odinetan Sanata Abdulaziz Musa Yar’adua wanda ya wakilci Sanata a yayin taron ya bayyana cewa manufar tallafawa manoman noman ita ce inganta noman ban ruwa a karamar hukumar Dutsin-Ma. Malam Zailani Muhammad ya tuna cewa ko a lokacin noman damina Sanata ‘Yar’aduwa ya samar da taki kyauta ga manoman yankin, ya kara da cewa baya ga bunkasa noma a yankin.

Sanata Abdulaziz Musa ‘Yar’aduwa ya samar da fitilun titi masu amfani da hasken rana da aka sanya a babban asibitin Dutsin-ma da manyan titunan garin domin inganta tsaro a yankin. Sanatan ya kuma horas da wasu matasa a yankin kan sanya hasken rana domin su zama masu dogaro da kai.

Manoman ban ruwa da suka ci gajiyar wannan karimcin sun nuna godiya ga Sanatan tare da bukace shi da ya gyara musu madatsar ruwa da ta lalace a shekarun baya sakamakon ambaliyar ruwa.

A madadin manoman da suka amfana, shugaban karamar hukumar Dutsin-Ma Hon. Sada Ibrahim Sada da mamba mai wakiltar karamar hukumar Dutsin-Ma a majalisar dokokin jihar Katsina Hon. Abubakar Muhammad Khamis wanda ya yi magana ta bakin wakilansu ya godewa Sanatan kan ayyukan ci gaban karamar hukumar Dutsin-Ma da jihar Katsina baki daya.

Sun bayyana Sanatan a matsayin nagartaccen wakilin jama’ar sa tare da rokonsa da ya ci gaba da gudanar da ayyukan alheri da yake.

  • Labarai masu alaka

    Labaran Hotuna: Gwamna Radda Ya Yi Wa ‘Yan Diflomasiyya 17 na Tarayyar Turai Bankwana Bayan Ziyarar Eid-el-Fitr Mai Cike Da Aiki

    Da fatan za a raba

    Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya yi wa ‘yan diflomasiyya 17 na Tarayyar Turai bankwana a filin jirgin saman Umaru Musa Yar’adua, Katsina, a ranar Lahadi, yayin da suka tashi zuwa Abuja, bayan kammala taron Eid-el-Fitr da Durbar a jihar.

    Kara karantawa

    ‘Katsina Ta Bada Ɗaya Daga Cikin Muhalli Mafi Kyau Na Nijeriya Don Zuba Jari Da Haɗin Gwiwa’ – Gwamna Radda Ga Wakilan Tarayyar Turai

    Da fatan za a raba

    Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, CON, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta himmatu wajen gina gwamnati mai haɗa kai da kuma samar da yanayi mai kyau don ci gaba mai ɗorewa da ci gaban tattalin arziki.

    Kara karantawa

    0 0 kuri'u
    Ƙimar Labari
    Subscribe
    Sanar da
    guest

    0 Sharhi
    Mafi tsufa
    Sabuwa Mafi Yawan Zabe
    Jawabin cikin layi
    Duba duk sharhi

    Labarai daga Jihohi

    ‘Yan Sanda Sun Kama Wanda Ake Zargi A Kan Iyakar Zamfara da Katsina Da Harsasai 800 AK-47 A Cikin Tankin Mai Na Babura

    ‘Yan Sanda Sun Kama Wanda Ake Zargi A Kan Iyakar Zamfara da Katsina Da Harsasai 800 AK-47 A Cikin Tankin Mai Na Babura

    Hukumar Kwastam ta Najeriya ta ziyarci hukumomin tsaro na ‘yan’uwa mata domin inganta hadin gwiwa tsakanin hukumomin da kuma tsaron kan iyakoki

    Hukumar Kwastam ta Najeriya ta ziyarci hukumomin tsaro na ‘yan’uwa mata domin inganta hadin gwiwa tsakanin hukumomin da kuma tsaron kan iyakoki
    0
    Bayyana tunanin ku kuma sami bayanai kyautax
    ()
    x